Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

A.m. 7:17-24 Littafi Mai Tsarki (HAU)

17. “Amma da lokacin cikar alkawarin da Allah ya yi wa Ibrahim ya gabato, jama'ar suka ƙaru, suka yawaita ƙwarai a ƙasar Masar,

18. har aka yi wani sarki a Masar, wanda bai san ko wane ne Yusufu ba.

19. Wannan sarki kuwa ya cuci kabilarmu, yana gwada wa kakanninmu tasku, yana sawa a yar da jariransu, don kada su rayu.

20. A lokacin nan ne aka haifi Musa, yaro kyakkyawan gaske. Sai aka rene shi wata uku a gidan ubansa.

21. Da aka yar da shi waje, 'yar Fir'auna ta ɗauke shi tallafinta, ta goya shi kamar ɗanta.

22. Sai aka karantar da Musa dukan ilimin Masarawa, shi kuwa mutum mai iko ne a cikin magana da ayyukansa.

23. “Yana gab da cika shekara arba'in ke nan, sai ya faɗo masa a rai yă ziyarci 'yan'uwansa Isra'ilawa.

24. Da ya ga ana cutar ɗayansu, ya tare wanda ake wulakantawa, ya rama masa, ya buge Bamasaren, ya mutu.

Karanta cikakken babi A.m. 7