Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

A.m. 7:12-20 Littafi Mai Tsarki (HAU)

12. Amma da Yakubu ya ji akwai alkama a Masar, ya aiki kakanninmu tafiyar farko.

13. A tafiyarsu ta biyu Yusufu ya sanar da kansa ga 'yan'uwansa, asalinsa kuma ya sanu ga Fir'auna.

14. Sai Yusufu ya aika wa ubansa Yakubu yă zo, da kuma dukan 'yan'uwansa, mutum saba'in da biyar.

15. Sai Yakubu ya tafi Masar. A can ma ya mutu, shi da kakanninmu.

16. Sai aka ɗebo su aka mai da su Shekem, aka sa su a kabarin da Ibrahim ya saya da kuɗi azurfa a wurin 'ya'yan Hamor a nan Shekem.

17. “Amma da lokacin cikar alkawarin da Allah ya yi wa Ibrahim ya gabato, jama'ar suka ƙaru, suka yawaita ƙwarai a ƙasar Masar,

18. har aka yi wani sarki a Masar, wanda bai san ko wane ne Yusufu ba.

19. Wannan sarki kuwa ya cuci kabilarmu, yana gwada wa kakanninmu tasku, yana sawa a yar da jariransu, don kada su rayu.

20. A lokacin nan ne aka haifi Musa, yaro kyakkyawan gaske. Sai aka rene shi wata uku a gidan ubansa.

Karanta cikakken babi A.m. 7