Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

A.m. 7:1-6 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Sai babban firist ya ce, “Ashe, haka ne?”

2. Sai Istifanas ya ce, “Ya ku 'yan'uwa da shugabanni, ku saurare ni. Allah Maɗaukaki ya bayyana ga kakanmu Ibrahim, sa'ad da yake ƙasar Bagadaza, tun bai zauna a Haran ba,

3. ya ce masa, ‘Tashi daga ƙasarku, daga kuma cikin 'yan'uwanka, ka je ƙasar da zan nuna maka.’

4. Sai ya tashi daga ƙasar Kaldiyawa, ya zauna a Haran. Daga can kuma, bayan mutuwar tsohonsa, Allah ya kawo shi ƙasar nan da yanzu kuke zaune.

5. Amma kuwa shi kansa, bai ba shi gādonta ba, ko da taki ɗaya, sai dai ya yi masa alkawari zai mallakar masa ita, shi da zuriyar bayansa, ko da yake ba shi da ɗa a lokacin.

6. Abin da Allah ya faɗa kuwa shi ne zuriyar Ibrahim za su yi baƙunci a wata ƙasa, mutanen ƙasar kuwa za su bautar da su, su kuma gwada musu tasku har shekara arbaminya.

Karanta cikakken babi A.m. 7