Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

A.m. 26:1-4 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Daga nan, sai Agaribas ya ce wa Bulus, “An ba ka izinin yin magana.”Sa'an nan fa Bulus ya ɗaga hannu, ya fara kawo hanzarinsa ya ce,

2. “Lalle na yi arziki, ya sarki Agaribas, da yake a gabanka ne zan kawo hanzarina yau a game da duk ƙarata da Yahudawa suka yi,

3. musamman da yake gwani ne kai ga sanin al'adun Yahudawa da maganganunsu. saboda haka, ina roƙonka ka saurare ni da haƙuri.

4. “Irin zaman da na yi tun daga ƙuruciyata, wato tun da farko, a cikin jama'armu da kuma a Urushalima har ya zuwa yau, sananne ne ga dukan Yahudawa.

Karanta cikakken babi A.m. 26