Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

A.m. 26:1-3 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Daga nan, sai Agaribas ya ce wa Bulus, “An ba ka izinin yin magana.”Sa'an nan fa Bulus ya ɗaga hannu, ya fara kawo hanzarinsa ya ce,

2. “Lalle na yi arziki, ya sarki Agaribas, da yake a gabanka ne zan kawo hanzarina yau a game da duk ƙarata da Yahudawa suka yi,

3. musamman da yake gwani ne kai ga sanin al'adun Yahudawa da maganganunsu. saboda haka, ina roƙonka ka saurare ni da haƙuri.

Karanta cikakken babi A.m. 26