Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

A.m. 20:18-22 Littafi Mai Tsarki (HAU)

18. Da suka zo wurinsa sai ya ce musu, “Ku da kanku kun san irin zaman da na yi a cikinku, tun ran da na sa ƙafata a ƙasar Asiya,

19. ina bauta wa Ubangiji da matuƙar tawali'u, har da hawaye, da gwaggwarmaya iri iri da na sha game da makircin Yahudawa.

20. Kun kuma san yadda ban ji nauyin sanar da ku kowane abu mai amfani ba, ina koya muku a sarari, da kuma gida gida,

21. ina tabbatar wa Yahudawa da al'ummai duka sosai wajibcin tuba ga Allah, da kuma gaskatawa da Ubangijinmu Yesu.

22. To, ga shi kuma, yanzu zan tafi Urushalima, Ruhu yana iza ni, ban kuwa san abin da zai same ni a can ba,

Karanta cikakken babi A.m. 20