Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

A.m. 15:36-41 Littafi Mai Tsarki (HAU)

36. An jima, Bulus ya ce wa Barnaba, “Bari yanzu mu koma mu dubo 'yan'uwa a kowane gari da muka sanar da Maganar Ubangiji, mu ga yadda suke.”

37. Barnaba kuwa ya so su tafi da Yahaya, wanda ake kira Markus.

38. Amma Bulus bai ga ya kyautu su tafi da wanda ya rabu da su a ƙasar Bamfiliya, ya ƙi tafiya aiki tare da su ba.

39. Sai matsanancin saɓanin ra'ayi ya auku, har ya kai su ga rabuwa. Barnaba ya ɗauki Markus, suka shiga jirgin ruwa zuwa tsibirin Kubrus,

40. amma Bulus ya zaɓi Sila, bayan 'yan'uwa sun yi masa addu'a alherin Allah ya kiyaye shi, ya tafi.

41. Bulus ya zazzaga ƙasar Suriya da ta Kilikiya, yana ta ƙarfafa Ikilisiyoyi.

Karanta cikakken babi A.m. 15