Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

A.m. 15:26-37 Littafi Mai Tsarki (HAU)

26. waɗanda suka sayar da ransu saboda sunan Ubangijinmu Yesu Almasihu.

27. Don haka, ga shi, mun aiko muku Yahuza da Sila, su ma za su gaya muku waɗannan abubuwa da bakinsu.

28. Domin Ruhu Mai Tsarki ya ga ya kyautu, mu ma mun gani, kada a ɗora muku wani nauyi fiye da na waɗannan abubuwa da suke wajibi, wato

29. ku guji abin da aka yanka wa gunki, da cin nama tare da jini, da cin abin da aka maƙure, da kuma fasikanci. In kun tsare kanku daga waɗannan, za ku zauna lafiya. Wassalam.”

30. Su kuma da aka sallame su, suka tafi Antakiya, da suka tara jama'ar, suka ba da wasiƙar.

31. Da suka karanta ta, suka yi farin ciki saboda gargaɗin.

32. Yahuza da Sila kuma, da yake su annabawa ne, suka gargaɗi 'yan'uwa da maganganu masu yawa, suka kuma ƙarfafa su.

33. Bayan sun yi 'yan kwanaki a wurin, sai 'yan'uwa su sallame su lafiya, suka koma wurin waɗanda suka aiko su.

34. [Amma Sila ya ga ya kyautu shi ya zauna a nan.]

35. Bulus da Barnaba kuwa suka dakata a Antakiya, suna koyarwa suna kuma yin bisharar Maganar Ubangiji, tare da waɗansu ma da yawa.

36. An jima, Bulus ya ce wa Barnaba, “Bari yanzu mu koma mu dubo 'yan'uwa a kowane gari da muka sanar da Maganar Ubangiji, mu ga yadda suke.”

37. Barnaba kuwa ya so su tafi da Yahaya, wanda ake kira Markus.

Karanta cikakken babi A.m. 15