Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

A.m. 15:13-20 Littafi Mai Tsarki (HAU)

13. Bayan sun gama jawabi, Yakubu ya amsa ya ce, “Ya ku 'yan'uwa, ku saurare ni.

14. Bitrus ya ba da labari yadda Allah ya fara kula da al'ummai, domin ya keɓe wata jama'a daga cikinsu ta zama tasa.

15. Wannan kuwa daidai yake da maganar annabawa, yadda yake a rubuce cewa,

16. ‘Bayan haka kuma zan komo,In sāke gina gidan Dawuda da ya rushe,In sāke ta da kangonsa,In tsai da shi,

17. Domin sauran mutane su nemi Ubangiji,Wato al'umman da suke nawa.’

18. Haka Ubangiji ya ce, shi da ya bayyana waɗannan abubuwa tun zamanin dā.

19. Saboda haka, a ganina, kada mu matsa wa al'ummai waɗanda suke juyowa ga Allah,

20. sai dai mu rubuta musu wasiƙa, su guji abubuwan ƙazanta na game da gumaka, da fasikanci, da cin abin da aka maƙure, da kuma cin nama tare da jini.

Karanta cikakken babi A.m. 15