Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

A.m. 10:17-29 Littafi Mai Tsarki (HAU)

17. Bitrus na a cikin damuwa ƙwarai a kan ko mece ce ma'anar wahayin da aka yi masa, sai ga mutanen da Karniliyas ya aiko tsaye a ƙofar zaure, sun riga sun tambayi gidan Saminu,

18. suna sallama, suna tambaya ko Saminu da ake kira Bitrus a nan ya sauka.

19. Tun Bitrus yana bibiya wahayin nan, Ruhu ya ce masa, “Ga mutum uku nan suna nemanka.

20. Tashi, ka sauka, ku tafi tare, ba da wata shakka ba, domin ni ne na aiko su.”

21. Sai Bitrus ya sauka wurin mutanen, ya ce musu, “Ga ni, ni ne kuke nema. Wace magana yake tafe da ku?”

22. Sai suka ce, “Wani jarumi ne, wai shi Karniliyas, mutumin kirki, mai tsoron Allah, wanda duk jama'ar Yahudawa suke yabo, shi ne wani tsattsarkan mala'ika ya umarce shi, ya aiko ka je gidansa, ya ji maganarka.”

23. Sai Bitrus ya shigo da su, ya sauke su.Kashegari ya tashi suka tafi tare, waɗansu 'yan'uwa kuma daga Yafa suka raka shi.

24. Kashegari kuma suka shiga Kaisariya. Dā ma Karniliyas na tsammaninsu, har ya gayyato 'yan'uwansa da aminansa.

25. Bitrus na shiga gidan ke nan sai Karniliyas ya tarye shi, ya fāɗi a gabansa, ya yi masa sujada.

26. Amma Bitrus ya tashe shi, ya ce, “Tashi, ai, ni ma ɗan adam ne.”

27. Bitrus na zance da shi, ya shiga ya tarar mutane da yawa sun taru.

28. Ya ce musu, “Ku da kanku kun sani, bai halatta Bayahude ya cuɗanya, ko ya ziyarci wani na wata kabila dabam ba. Amma Allah ya nuna mini kada in ce da kowa marar tsarki, ko mai ƙazanta.

29. Saboda haka da aka neme ni, na zo, ban ce a'a ba. To, yanzu ina so in ji abin da ya sa kuka kira ni.”

Karanta cikakken babi A.m. 10