Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

A.m. 10:13-19 Littafi Mai Tsarki (HAU)

13. Sai ya ji wata murya ta ce masa, “Bitrus, tashi, ka yanka ka ci.”

14. Amma Bitrus ya ce, “A'a, ya Ubangiji, don ban taɓa cin wani abu marar tsarki ko mai ƙazanta ba.”

15. Sai ya sāke jin murya, ji na biyu, ta ce, “Abin da Allah ya tsarkake, kada ka ce da shi marar tsarki.”

16. Da an yi wannan sau uku, nan da nan aka yi sama da abin.

17. Bitrus na a cikin damuwa ƙwarai a kan ko mece ce ma'anar wahayin da aka yi masa, sai ga mutanen da Karniliyas ya aiko tsaye a ƙofar zaure, sun riga sun tambayi gidan Saminu,

18. suna sallama, suna tambaya ko Saminu da ake kira Bitrus a nan ya sauka.

19. Tun Bitrus yana bibiya wahayin nan, Ruhu ya ce masa, “Ga mutum uku nan suna nemanka.

Karanta cikakken babi A.m. 10