Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Afi 5:16-29 Littafi Mai Tsarki (HAU)

16. Ku yi matuƙar amfani da lokaci don kwanaki mugaye ne.

17. Don haka kada ku zama marasa azanci, sai dai ku fahimci abin da yake nufin Ubangiji.

18. Kada kuma ku bugu da giya, hanyar masha'a ke nan. Sai dai ku cika da Ruhu,

19. kuna zance da junanku da kalmomin zabura, da waƙoƙin yabo, da waƙoƙi na ruhu, kuna raira waƙoƙi da zabura ga Ubangiji da yabo a zukatanku.

20. Kullum ku riƙa gode wa Allah Uba da sunan Ubangijinmu Yesu Almasihu a kan ko mene ne.

21. Ku bi juna saboda ganin girman Almasihu.

22. Ku matan aure, ku yi biyayya ga mazanku, Ubangiji ke nan kuke yi wa.

23. Don miji shi ne shugaban matarsa, kamar yadda Almasihu yake shugaban Ikkilisiya, wato, jikinsa, shi kansa kuma shi ne Mai Ceton jikin.

24. Kamar yadda Ikkilisiya take bin Almasihu, haka kuma mata su bi mazansu ta kowane hali.

25. Ku maza, ku ƙaunaci matanku kamar yadda Almasihu ya ƙaunaci ikkilisiya, har ya ba da kansa dominta,

26. domin ya miƙa ta ga Allah, tsarkakakkiya bayan da ya wanke ta da ruwa ta wurin Kalma,

27. domin shi kansa yă ba kansa Ikkilisiya da ɗaukakarta, ba tare da tabo ko tamoji ba, ko wani irin abu haka, tă dai zamo tsattsarka marar aibu.

28. Ta haka ya wajaba maza su ƙaunaci matansu, jikinsu ke nan suke yi wa. Ai, wanda ya ƙaunaci matarsa, ya ƙaunaci kansa ke nan.

29. Domin ba wanda ya taɓa ƙin jikinsa, sai dai ya rene shi, ya yi tattalinsa, kamar yadda Almasihu yake yi wa Ikkilisiya,

Karanta cikakken babi Afi 5