Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

2 Tim 2:8-12 Littafi Mai Tsarki (HAU)

8. Ka tuna da Yesu Almasihu fa, shi da aka tashe shi daga matattu, na zuriyar Dawuda bisa ga bisharata,

9. wadda nake shan wuya saboda ita, har nake ɗaure kamar mai laifi. Amma Maganar Allah ba a ɗaure take ba.

10. Don haka nake jure kome saboda zaɓaɓɓu, domin su ma su sami ceton nan da yake samuwa ta wurin Almasihu, a game da madawwamiyar ɗaukaka.

11. Maganar nan tabbatacciya ce,“In mun mutu tare da shi, za mu rayu ma tare da shi,

12. In mun jure, za mu yi mulki ma tare da shi,In mun yi musun saninsa, shi ma zai yi musun saninmu,

Karanta cikakken babi 2 Tim 2