Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

2 Kor 8:8-19 Littafi Mai Tsarki (HAU)

8. Ba kallafa muku wannan nake yi ba, sai dai ta nuna himmar waɗansu, in tabbata ƙaunarku ma sahihiya ce.

9. Domin kun san alherin Ubangijinmu Yesu Almasihu, ko da yake shi mawadaci ne, sai ya zama matalauci sabili da ku, domin ta wurin talaucinsa ku wadata.

10. A wannan al'amari, ga shawarata. Ai, ya fiye muku a yanzu ku ƙarasa abin da kuka fara yi a bara, har kuka yi da ra'inku.

11. To, sai ku ƙarasa aikin da irin ra'in da kuka fara, gwargwadon ikonku.

12. Domin mutum yana da niyyar bayarwa, bayarwarsa za ta zama abar karɓa ce, bisa ga yawan abin da yake da shi, ba bisa ga abin da ba shi da shi ba.

13. Ba nufi nake yi a sawwaƙe wa waɗansu, ku kuwa a jibga muku nauyin ba.

14. Amma don a raba daidai wa daida, sai ku taimake su a yanzu da yalwarku saboda rashinsu, don wata rana su ma su taimake ku da yalwarsu saboda rashinku, don a daidaita al'amari.

15. Yadda yake a rubuce cewa, “Wanda ya tara mai yawa, bai fi bukatarsa ba, wanda ya tara kaɗan kuwa, ba abin da ya gaza masa.”

16. Godiya tā tabbata ga Allah wanda ya sa tsananin kula da ku a zuciyar Titus, kamar yadda nake yi.

17. Ba kuwa na'am da roƙonmu kaɗai ya yi ba, har ma saboda tsananin himma tasa yana zuwa wurinku da ra'in kansa.

18. Ga shi, mun aiko ɗan'uwan nan tare da shi, wanda ya yi suna wajen yin bishara a dukan ikilisiyoyi,

19. ba kuwa haka kaɗai ba, har ma ikilisiyoyi sun zaɓe shi ya riƙa tafiya tare da mu kan wannan aikin alheri da muke yi saboda ɗaukakar Ubangiji, da kuma nuna kyakkyawar niyyarmu.

Karanta cikakken babi 2 Kor 8