Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

2 Kor 11:28-31 Littafi Mai Tsarki (HAU)

28. Banda waɗansu abubuwa dabam kuma, kowace rana ina a matse da matsananciyar kula saboda dukan ikilisiyoyi.

29. Wane ne ya raunana da ban raunana ba? Wane ne aka sa tuntuɓe, ban ji zafin ba?

30. In ma lalle ne in yi gadara, to, sai in yi taƙama da abubuwan da suke nuna raunanata.

31. Allahn Ubangiji Yesu, wato Ubansa, wanda ya yabo ya tabbata a gare shi har abada, ya sani ba ƙarya nake yi ba.

Karanta cikakken babi 2 Kor 11