Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

2 Kor 1:22-24 Littafi Mai Tsarki (HAU)

22. Ya buga mana hatiminsa cewa mu nasa ne, ya kuma yi mana baiwa da Ruhunsa a zukatanmu, domin tabbatar da abin da zai yi a nan gaba.

23. Labudda, Allah shi ne mashaidina a kan cewa, musamman don sawwaƙe muku ne, na fāsa zuwa Koranti.

24. Ba cewa muna nuna muku iko a kan bangaskiyarku ba ne, a'a, sai dai muna aiki tare ne, domin ku yi farin ciki, domin a game da bangaskiyarmu kam, kuna tsaye kankan.

Karanta cikakken babi 2 Kor 1