Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

1 Yah 3:19-23 Littafi Mai Tsarki (HAU)

19. Ta haka za mu tabbata mu na gaskiya ne, har kuma mu amince wa kanmu gaban Allah,

20. duk sa'ad da zuciyarmu ta ba mu laifi, saboda Allah ya fi ta, ya kuma san kome.

21. Ya ku ƙaunatattuna, in zuciyarmu ba ta ba mu laifi ba, sai mu je gaban Allah amincewa.

22. Mukan kuma sami duk abin da muka roƙa a gare shi, domin muna bin umarninsa, muna kuma yin abin da yake so.

23. Umarninsa kuwa shi ne mu gaskata da sunan Ɗansa Yesu Almasihu, mu kuma ƙaunaci juna, kamar yadda ya umarce mu.

Karanta cikakken babi 1 Yah 3