Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

1 Tim 6:1-2 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Duk ɗaukacin masu igiyar bauta a wuyansu, su ɗauki iyayengijinsu a kan sun cancanci a girmama su matuƙa, don kada a ɓata sunan Allah da kuma koyarwar nan.

2. Waɗanda suke da iyayengiji masu ba da gaskiya, kada su raina su, domin su 'yan'uwa ne a gare su. Sai ma su ƙara bauta musu, tun da yake waɗanda suke moron aikin nan nasu masu ba da gaskiya ne, ƙaunatattu kuma a gare su.Ka koyar da waɗannan abubuwa, ka kuma yi gargaɗinsu.

Karanta cikakken babi 1 Tim 6