Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

1 Tim 1:6-14 Littafi Mai Tsarki (HAU)

6. Waɗansu sun kauce wa waɗannan al'amura, har sun bauɗe, sun shiga zancen banza.

7. Suna burin zama masanan Attaura, ba tare da fahimtar abin da suke faɗa ba, balle matsalar da suke taƙamar haƙiƙicewa a kai.

8. To, mun san Shari'a aba ce mai kyau, in mutum ya yi aiki da ita yadda ya wajaba,

9. yana kuma tunawa, cewa ita Shari'a ba a kafa ta domin masu adalci ba, sai dai kangararru, da marasa biyayya, da marasa bin Allah, da masu zunubi, da marasa tsarkaka, da masu saɓon Allah, da masu kashe iyaye maza da mata, da masu kisankai,

10. da fasikai, da masu luɗu, da masu sace mutane, da maƙaryata, da masu shaidar zur, da kuma duk sauran abin da ya sāɓa sahihiyar koyarwar nan,

11. bisa ga bishara mai daraja ta Allah abar yabo, wadda aka danƙa mini.

12. Ina gode wa Almasihu Yesu Ubangijinmu, wanda ya ƙarfafa ni, saboda ya amince da ni, har ya sa ni aikinsa,

13. ko da yake dā can sāɓo nake yi, ina tsanantarwa, ina wulakantarwa, duk da haka, sai dai aka yi mini jinƙai, domin na yi haka ne da jahilci saboda rashin bangaskiya.

14. Alherin Ubangijinmu kuma ya kwararo mini ƙwarai da gaske, a game da bangaskiya, da kuma ƙaunar da take ga Almasihu Yesu.

Karanta cikakken babi 1 Tim 1