Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

1 Tas 5:14-21 Littafi Mai Tsarki (HAU)

14. Muna kuma yi muku gargaɗi, 'yan'uwa, ku tsawata wa malalata, ku ƙarfafa masu rarraunar zuciya, ku taimaki marasa tsayayyiyar zuciya, ku yi haƙuri da kowa da kowa.

15. Ku lura fa, kada kowa ya rama mugunta da mugunta. Sai dai kullum ku nace yi wa juna aiki nagari, da kuma dukkan mutane.

16. Ku riƙa yin farin ciki a kullum.

17. Ku riƙa yin addu'a ba fāsawa.

18. Ku godiya ga Allah a kowane hali, domin shi ne nufin Allah a game da ku ta wurin Almasihu Yesu.

19. Kada ku danne maganar Ruhu.

20. Kada ku raina annabci,

21. sai dai ku jarraba kome, ku riƙi abin da yake nagari kankan.

Karanta cikakken babi 1 Tas 5