Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

1 Kor 15:22-27 Littafi Mai Tsarki (HAU)

22. Kamar yadda duk ake mutuwa saboda Adamu, haka duk za a rayar da su saboda Almasihu.

23. Amma kowanne bi da bi, Almasihu ne nunan fari, sa'an nan a ranar komowarsa, waɗanda suke na Almasihu.

24. Sa'an nan sai ƙarshen, sa'ad da zai mayar wa Allah Uba mulki, bayan ya shafe dukkan sarauta da mulki da iko.

25. Domin kuwa lalle ne ya yi mulki, har ya take dukkan maƙiyansa.

26. Magabciyar ƙarshe da za a shafe, ita ce mutuwa.

27. “Gama Allah ya sarayar da kome a ƙarƙashin ikonsa.” Amma da aka ce, “An sarayar da kome karƙashin ikonsa” a fili yake shi wannan da ya sarayar da kome a ƙarƙashin ikonsa ɗin, a keɓe yake.

Karanta cikakken babi 1 Kor 15