Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

1 Kor 14:35-40 Littafi Mai Tsarki (HAU)

35. In akwai wani abin da suke so su sani, to, sai su tambayi mazansu a gida, don abin kunya ne mace ta yi magana a cikin taron ikkilisiya.

36. A kanku ne maganar Allah ta fara, ko kuwa a gare ku kaɗai ta isa?

37. In wani yana zato shi annabi ne, ko kuwa mai wata baiwa ta ruhu, to, sai yă fahimta, abin nan da nake rubuto muku umarni ne na Ubangiji.

38. In kuwa wani ya ƙi kula da wannan, shi ma sai a ƙi kula da shi.

39. Saboda haka, 'yan'uwa, sai ku himmantu ga samun baiwar yin annabci, kada kuma ku hana yin magana da waɗansu harsuna.

40. Sai dai a yi kome ta hanyar da ta dace, a shirye kuma.

Karanta cikakken babi 1 Kor 14