Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

1 Bit 3:9-20 Littafi Mai Tsarki (HAU)

9. Kada ku rama mugunta da mugunta, ko zagi da zagi, a maimakon haka, sai ku sa albarka. Domin a kan haka ne musamman aka kira ku, ku kuma gaji albarka.

10. Domin,“Duk mai so ya more wa zamansa na duniya da alheri,Sai ya kame bakinsa daga ɓarna,Ya kuma hana shi maganar yaudara.

11. Ya rabu da mugunta,ya kama nagarta,Ya himmantu ga zaman lafiya, ya kuma dimance ta.

12. Gama Ubangiji yana lura da masu aikata adalci,Yana kuma sauraron roƙonsu.Amma Ubangiji yana gāba da masu aikata mugunta.”

13. To, wa zai cuce ku in kun himmantu a kan abin da yake nagari?

14. Amma ko da za ku sha wuya saboda aikata abin da yake daidai, ku masu albarka ne. Kada ku ji tsoronsu, kada kuma ku damu.

15. Sai dai ku girmama Almasihu a zukatanku da hakikancewa, shi Ubangiji ne. Kullum ku zauna a shirye ku ba da amsa ga duk wanda ya tambaye ku dalilin begen nan naku, amma fa da tawali'u da bangirma.

16. Ku kuma kasance da lamiri mai kyau, don in an zage ku, waɗanda suka kushe kyakkyawan halinku na bin Almasihu su kunyata.

17. Zai fi kyau a sha wuya ga yin abin da yake nagari, in haka nufin Allah ne, da a sha don yin abin da ba daidai ba.

18. Domin Almasihu ma ya mutu sau ɗaya tak ba ƙari, domin kawar da zunubanmu, mai adalci saboda marasa adalci, domin ya kai mu ga Allah. An kashe shi a jiki, amma an rayar da shi a ruhu.

19. Da ruhun ne kuma ya je ya yi wa ruhohin da suke a kurkuku shela,

20. wato, waɗanda dā ba su bi ba, sa'ad da Allah ya yi jira da haƙuri a zamanin Nuhu, a lokacin sassaƙar jirgin nan, wanda a cikinsa mutane kaɗan, wato takwas suka kuɓuta ta ruwa.

Karanta cikakken babi 1 Bit 3