Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

1 Bit 1:20-25 Littafi Mai Tsarki (HAU)

20. An rigyasaninsa a kan haka, tun ba a halicci duniya ba, amma saboda ku ne aka bayyana shi a zamanin ƙarshe.

21. To gare shi ne kuka gaskata da Allah, wanda ya ta da shi daga matattu, ya kuma ɗaukaka shi, domin bangaskiyarku da begenku su kasance ga Allah.

22. Da yake kun tsarkake ranku kuna yi wa gaskiya biyayya har kuna nuna sahihiyar ƙauna ga 'yan'uwa, sai ku himmantu ga ƙaunar juna da zuciya ɗaya.

23. Gama sāke haifuwarku aka yi, ba ta iri mai lalacewa ba, sai dai marar lalacewa, wato, ta Maganar Allah rayayyiya dawwamammiya.

24. Domin“Duk ɗan adam kamar ciyawa yake,Duk darajarsa kamar furen ciyawa take,Ciyawar takan bushe, furen yakan kaɗe,

25. Maganar Ubangiji kuwa dawwamammiya ce,”Ita ce maganar bishara da aka yi muku.

Karanta cikakken babi 1 Bit 1