Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

1 Bit 1:18-25 Littafi Mai Tsarki (HAU)

18. Domin kun sani an fanshe ku ne daga al'adunku na banza da wofi da kuka gāda, ba da abubuwa masu lalacewa kamar azurfa da zinariya ba,

19. sai dai da jinin nan mai daraja na Almasihu, kamar na ɗan rago marar naƙasa, marar tabo.

20. An rigyasaninsa a kan haka, tun ba a halicci duniya ba, amma saboda ku ne aka bayyana shi a zamanin ƙarshe.

21. To gare shi ne kuka gaskata da Allah, wanda ya ta da shi daga matattu, ya kuma ɗaukaka shi, domin bangaskiyarku da begenku su kasance ga Allah.

22. Da yake kun tsarkake ranku kuna yi wa gaskiya biyayya har kuna nuna sahihiyar ƙauna ga 'yan'uwa, sai ku himmantu ga ƙaunar juna da zuciya ɗaya.

23. Gama sāke haifuwarku aka yi, ba ta iri mai lalacewa ba, sai dai marar lalacewa, wato, ta Maganar Allah rayayyiya dawwamammiya.

24. Domin“Duk ɗan adam kamar ciyawa yake,Duk darajarsa kamar furen ciyawa take,Ciyawar takan bushe, furen yakan kaɗe,

25. Maganar Ubangiji kuwa dawwamammiya ce,”Ita ce maganar bishara da aka yi muku.

Karanta cikakken babi 1 Bit 1