Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Kol 4:14-18 Littafi Mai Tsarki (HAU)

14. Luka, ƙaunataccen likitan nan, da Dimas suna gaishe ku.

15. A gayar mini da 'yan'uwa na Lawudikiya, da kuma Nimfa da ikilisiyar da take taruwa a gidanta.

16. Sa'ad da aka karanta wasiƙar nan a gabanku, ku sa a karanta ta kuma a gaban ikilisiyar da take a Lawudikiya, ku kuma ku karanta tasu, wato ta Lawudikiyawa.

17. Ku kuma faɗa wa Arkibus ya mai da hankali ya cika hidimar da Ubangiji ya sa shi.

18. Ni Bulus, ni nake rubuta gaisuwar nan da hannuna. Ku tuna da ɗaurina. Alheri yă tabbata a gare ku.

Karanta cikakken babi Kol 4