19. Wannan sarki kuwa ya cuci kabilarmu, yana gwada wa kakanninmu tasku, yana sawa a yar da jariransu, don kada su rayu.
20. A lokacin nan ne aka haifi Musa, yaro kyakkyawan gaske. Sai aka rene shi wata uku a gidan ubansa.
21. Da aka yar da shi waje, 'yar Fir'auna ta ɗauke shi tallafinta, ta goya shi kamar ɗanta.